04/02/2021
El-Rufa'i ya yi kira ga sauran gwamnoni da su yi tir da hare-haren ƙabilanci
Gwamnatin jihar Kaduna ta fitar da wata sanarwa da ke tir da wasu bidiyo da ake yadawa a shafuka sada zumunta mai nuna inda ake kashe ƴan wasu ƙabila da lalata gidaje a wasu sassan Najeriya.
Sanarwar mai dauke da sa hannun gwamnan jihar, Malam Nasir Ahmed El-Rufa'i ya ce yana takaicin mummunan tasirin da waɗannan hotunan za su yi musamman ga zaman lafiya kasar.
Ya kuma yi kira ga dukka ƴan Najeriya masu zama a jiharsa da su zama masu bin doka da kare hakkin abokan zamansu.
Gwamna El-Rufa'i ya ja hankalin takwarorinsa na sauran jihohi da su yi kira irin nasa sannan su yi alla-wadai da irin waɗannan hare-haren.
"Dole ne mu guji tashin hankali kuma mu zama masu bin dokoki a duk inda mu ke. Mun ga sharrin irin waɗannan hare-haren, wannna ya jawo abubuwa da dama k**a da karuwar aikta manyan laifuka da mace-mace," a cewarsa.
El-Rufa'i ya ce bai dace a ce ana ware ƴan wata kabila ko addini a laƙaba masu wani laifi ba.
"Shi ya a ma a jiharmu a shekrarar 2017 muka umarci k**a mutanen da s**a kori ƴan wasu kabila daga jiharmu," a cewar gwamnan.
Ya ce faragar da mutane ke ciki a fadin kasar nan saboda matsalolin tsaro, ya sa ya zama tilas shugabanni su dauki matakan hana aikata manyan laifuka da cin zarafin mutane.
Ya kuma yi kira ga 'yan majalisar dokokin Najeriya da su gaggauta sauya dokokin kundin tsarin mulki da za su samar da 'yan sanda jiha saboda a cewarsa wannan ne kawai zai tabbatar da bin doka a kasar baki daya.
Ya ce jiharsa ba za ta taba lamunta zargi ga mutanen da ba su ji b, ba su gani ba, ana dora masu laifukan da ba su aikata saboda kawai kasancewarsu 'yan wani bangare na Najeriya.