Nagarta Radio Kaduna

Nagarta Radio Kaduna Nagarta Radio muryar haɗa kan jama'a
(2)

Rikicin cikin gida a jam’iyyar APC a Jihar Kaduna ya ƙara tsananta bayan musayar kalamai da zarge-zarge tsakanin tsohon ...
01/06/2026

Rikicin cikin gida a jam’iyyar APC a Jihar Kaduna ya ƙara tsananta bayan musayar kalamai da zarge-zarge tsakanin tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Yusuf Ibrahim Zailani, da Babban Mai Bai Wa Gwamna Uba Sani Shawara Kan Harkokin Siyasa, Muhammad Abubakar Mamadi.

Zailani ya zargi wasu shugabannin jam’iyyar da yin maguɗi a zaɓukan fidda gwani na APC tare da yaudarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan wasu batutuwan siyasa. Ya yi gargaɗin cewa irin waɗannan abubuwa na iya raunana jam’iyyar kafin zaɓuɓɓuka masu zuwa.

Sai dai a martaninsa, Muhammad Abubakar Mamadi ya ƙaryata wasu daga cikin zarge-zargen, yana mai cewa shi da Zailani tare da wasu mutane sun taɓa rubuta sakamakon zaɓe a Ƙaramar Hukumar Igabi a baya.

Mamadi ya kuma yi wani zargi mai ɗaukar hankali inda ya ce akwai lokacin da shi da Zailani s**a gudu tare bayan da ‘yan sanda s**a fara nemansu. Wannan ikirari ya ƙara jawo hankalin jama’a kan rikicin da ke tsakanin ‘yan siyasar biyu.

Har ila yau, Mamadi ya yi iƙirarin cewa s**ar da Zailani ke yi wa wasu shugabannin APC na da alaƙa da rasa tasirin siyasa da yake da shi a cikin jam’iyyar.

Musayar zarge-zargen ta haifar da martani daban-daban daga jama’a tare da sake tayar da tambayoyi kan sahihancin wasu zaɓukan da aka gudanar a baya a jihar.

Rahotanni na nuni da cewa rikicin na ci gaba da ɗaukar sabon salo yayin da bangarorin ke ci gaba da bayyana matsayinsu a bainar jama’a.

01/06/2026

Shirin Kowa Ya Iya Allonsa na Litinin, 1 ga Yuni, 2026,

Bako:
🎤Engr. Inuwa Ibrahim, (Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna.)

Maudu'i:
• Nasarori da ayyukan da Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna ta samu a ƙarƙashin jagorancinsa.

• Cikar Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, shekaru uku a kan karagar mulki da irin ci gaban da aka samu a fannin sufuri.

🎙️Mai Gabatarwa:
Aminu Adamu Fasataya.

Yayin da siyasar 2027 ke ƙara ɗaukar zafi, wa kuke ganin ya dace ya jagoranci Nijeriya a matsayin Shugaban Ƙasa?A - Atik...
01/06/2026

Yayin da siyasar 2027 ke ƙara ɗaukar zafi, wa kuke ganin ya dace ya jagoranci Nijeriya a matsayin Shugaban Ƙasa?

A - Atiku Abubakar ?
B - Bola Ahmed Tinubu?
C - GoodLuck Jonathan?
D - Peter Obi?

Ku bayyana ra'ayoyinku.

🔊SANARWAShirin Kowa Ya Iya Allonsa na gobe Litinin, 1 ga Yuni, 2026, idan Allah ya so zai karɓi baƙuncin 👇🎤Engr. Inuwa I...
31/05/2026

🔊SANARWA

Shirin Kowa Ya Iya Allonsa na gobe Litinin, 1 ga Yuni, 2026, idan Allah ya so zai karɓi baƙuncin 👇

🎤Engr. Inuwa Ibrahim, (Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna.)

A yayin shirin, za a tattauna kan:

• Nasarori da ayyukan da Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna ta samu a ƙarƙashin jagorancinsa.

• Cikar Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, shekaru uku a kan karagar mulki da irin ci gaban da aka samu a fannin sufuri.

Lokaci: 11:00 na safe

Ku kasance tare da mu domin sauraron cikakken shirin.

🎙️Mai Gabatarwa:
Aminu Adamu Fasataya.

Masu Ruwa da Tsaki na magoya bayan ADC a Kaduna ta Arewa Sun Yi Watsi da Sakamakon Zaɓen Fidda Gwani na Sanata, Sun Nemi...
31/05/2026

Masu Ruwa da Tsaki na magoya bayan ADC a Kaduna ta Arewa Sun Yi Watsi da Sakamakon Zaɓen Fidda Gwani na Sanata, Sun Nemi A Sake Duba Tsarin

Wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Shiyya ta Ɗaya (Kaduna ta Arewa) sun yi watsi da sakamakon zaɓen fidda gwani na kujerar Sanatan Kaduna ta Arewa da aka gudanar a ranar 30 ga Mayu, 2026, inda aka ayyana Alhaji Khalid Mustapha a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.

A wani taron manema labarai da s**a gudanar a Kaduna ranar Asabar, ƙarƙashin inuwar ADC Stakeholders Support Forum, Zone One, masu ruwa da tsakin sun bayyana cewa zaɓen bai gudana bisa ƙa’idoji, dokoki da tsarin dimokuraɗiyya na jam’iyyar ba.

Ƙungiyar ta nuna damuwa kan abin da ta kira rashin gaskiya, adalci da bin ka’ida a tsarin zaɓen, tana mai zargin cewa an hana Sanata Suleiman Abdu Kwari damar shiga takarar duk da cewa ya cika sharuddan da jam’iyyar ta gindaya.

Sun ce Sanata Kwari ya tsallake tantancewar da jam’iyyar ta gudanar a matakin ƙasa kuma an tabbatar da cancantarsa ta shiga zaɓen, don haka suna tambayar dalilin da ya sa kwamitin zaɓen fidda gwani ya cire shi daga takarar.

Masu ruwa da tsakin sun kuma yi iƙirarin cewa zargin aikata ayyukan da s**a saɓa wa jam’iyya da aka danganta wa Sanata Kwari ba hujja ba ce da kwamitin zaɓen fidda gwani zai iya amfani da ita wajen hana shi shiga takara, domin a cewarsu irin wannan hukunci yana ƙarƙashin ikon hukumomin jam’iyyar da s**a dace.

Ƙungiyar ta buƙaci shugabancin ADC na ƙasa, Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) da kuma shugabannin jam’iyyar a Jihar Kaduna da su gaggauta bincike tare da sake duba yadda aka gudanar da zaɓen domin magance korafe-korafen da aka gabatar.

Sun ce matakin zai taimaka wajen dawo da amincewar mambobin jam’iyyar da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyya a cikin gida.

A ƙarshe, ƙungiyar ta sake jaddada cewa ba ta amince da sakamakon zaɓen fidda gwani na Sanatan Kaduna ta Arewa ba, tare da kira ga hukumomin jam’iyyar su ɗauki matakin da ya dace domin tabbatar da adalci, gaskiya da haɗin kai a tsakanin mambobi.

Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya gargadi ‘yan siyasa da su guji amfani da siyasa wajen kawo cikas ga zaman lafiyar ...
30/05/2026

Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya gargadi ‘yan siyasa da su guji amfani da siyasa wajen kawo cikas ga zaman lafiyar da ake morewa a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin ziyarar gaisuwar Sallah da ya kai wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, a fadarsa yayin bikin Eid-el-Kabir.

Ahmed Aliyu ya ce gwamnatin jihar ba za ta bari wasu su kawo cikas ga zaman lafiya da haɗin kan al’umma ba, yana mai cewa za a hukunta duk wanda aka samu yana lalata kadarorin gwamnati.

Ya kuma tabbatar da ci gaba da bai wa jami’an tsaro goyon baya wajen yaƙi da ‘yan bindiga, tare da bayyana masu bai wa ‘yan bindiga bayanai a matsayin babban ƙalubale ga tsaro.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati za ta gabatar da kudirin doka a majalisar jihar domin tanadar hukunci ga masu bai wa ‘yan bindiga bayanai.

A nasa jawabin, Sarkin Musulmi ya buƙaci a gudanar da siyasa cikin lumana yayin da ake shirin fara yakin neman zaɓe, tare da yabawa gwamnatin Ahmed Aliyu kan ayyukan raya ƙasa da bunƙasa harkokin addinin Musulunci a jihar.

Ƙungiyar ADC Kaduna Youth Vanguard Support Group (Zone One) ta bayyana damuwarta kan rahotannin da ke cewa ana shirin ci...
30/05/2026

Ƙungiyar ADC Kaduna Youth Vanguard Support Group (Zone One) ta bayyana damuwarta kan rahotannin da ke cewa ana shirin cire Sanata Suleiman Abdu Kwari daga takarar fidda gwani ta Sanatan Kaduna ta Arewa a jam’iyyar ADC.

A wani taron manema labarai da ƙungiyar ta gudanar a ranar 30 ga Mayu, 2026, ta ce akwai alamun rashin gaskiya da nuna son kai a tsarin gudanar da zaɓen fidda gwanin.

Ƙungiyar ta tuna cewa tun a ranar 29 ga Mayu, Sanata Suleiman Abdu Kwari ya bayyana rashin samun wata sanarwa a hukumance dangane da sauya ranar zaɓen fidda gwani, tare da neman a fito da cikakkun bayanai kan ranar zaɓe, wurin gudanarwa, tsarin tantance wakilai da jerin masu kada ƙuri’a.

Sai dai, maimakon warware waɗannan matsaloli, ƙungiyar ta ce yanzu ana ta samun rahotannin da ke nuna cewa akwai wani yunƙuri na hana shi shiga takarar gaba ɗaya.

Ƙungiyar ta ce hakan ya haifar da zargin cewa wasu masu ruwa da tsaki a jam’iyyar na ƙoƙarin tabbatar da nasarar Sanata mai ci yanzu, Ibrahim Khalid Soba, wanda kwanan nan ya koma jam’iyyar ADC.

Sai dai ƙungiyar ta jaddada cewa ba ta da matsala da Sanata Soba ko wata takara tasa, amma tana adawa da duk wani yunƙuri na fifita wani ɗan takara fiye da sauran masu neman takara.

Ƙungiyar ta kuma nuna damuwa kan rahoton da ake cewa ya ba da shawarar cire Suleiman Abdu Kwari daga takara, tana mai cewa babu wasu hujjoji karara da aka gabatar domin tabbatar da zarge-zargen da ake yi masa.

Ta ce abin mamaki ne yadda aka fara tantance Sanatan tare da amincewa da takararsa, amma daga baya ba tare da bayyana wani sabon dalili ba ake son sauya matsayar.

Ƙungiyar ta yi gargadin cewa duk wani yunƙuri na gudanar da zaɓe tare da cire wasu ’yan takara ba bisa ƙa’ida ba zai iya janyo rikici da ƙalubalen shari’a a cikin jam’iyyar.

A ƙarshe, ƙungiyar ta ce tana goyon bayan bukatar Sanata Suleiman Abdu Kwari na ganin an gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya, inda wakilai za su

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Nijeriya na cikin wani yanayi na jarabawa da ƙalubale, kamar yadda saura...
29/05/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Nijeriya na cikin wani yanayi na jarabawa da ƙalubale, kamar yadda sauran ƙasashe s**a fuskanta kafin samun ci gaba mai ɗorewa.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin jawabinsa na cika shekara uku da hawa mulki, inda ya ce yana da tabbacin cewa Nijeriya za ta shawo kan matsalolin da take ciki tare da samun ƙarfi, haɗin kai da wadata a nan gaba.

Ya ce al’ummai da dama sun fuskanci jarabawa kafin su kai ga ɗaukaka, don haka a yanzu Nijeriya ma na cikin irin wannan lokaci a yau, amma da yaƙinin cewa za a fito daga wannan hali cikin ƙarfi da ci gaba.

Rukuni Na Biyar Na Wankan Sallan Masu Bibiyar Shafin Nagarta Radio Kaduna. Za Mu Ci Gaba Da Wallafa Hotunan Sannu A Hank...
28/05/2026

Rukuni Na Biyar Na Wankan Sallan Masu Bibiyar Shafin Nagarta Radio Kaduna.

Za Mu Ci Gaba Da Wallafa Hotunan Sannu A Hankali

Address

Katabu, Mararaban Jos Kaduna
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nagarta Radio Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share