18/01/2026
SANARWAR GA MANEMA LABARAI
CPSST TA YI ALLAH-WADAI DA KAKKAUSAN SUKAR KISAN UWA DA ’YA’YANTA SHIDA A JIHAR KANO
Cibiyar Zaman Lafiya, Dorewar Ci Gaba da Jure Bambancin Ra’ayi (CPSST) na nuna matuƙar alhini, girgiza da kuma ɓacin rai game da kisan gilla da aka yi wa wata uwa tare da ’ya’yanta shida a Jihar Kano. Wannan mugun aiki na rashin imani ya tauye martabar ɗan Adam kuma ya nuna girman barazanar da ke fuskantar rayukan fararen hula a cikin al’umma.
CPSST na yin Allah-wadai da wannan aika-aika, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan, al’ummar Jihar Kano, da dukkan ’yan Najeriya da ke jimami wannan mummunan al’amari. Kisan yara marasa laifi da mahaifiyarsu ba shi da wani uzuri a kowane hali, kuma dole ne a tabbatar an hukunta masu laifin.
Muna kira ga hukumomin tsaro da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da bincike mai zurfi, gaskiya, kuma cikin gaggawa, domin gano tare da cafke masu hannu a wannan kisa, a gurfanar da su gaban kuliya bisa doka. Dole ne a tabbatar da adalci domin dawo da amincewar jama’a da kuma hana sake faruwar irin wannan ta’asa.
CPSST kuma na roƙon shugabannin al’umma, malaman addini, da ƙungiyoyin farar hula da su ƙara himma wajen inganta zaman lafiya, jure bambancin ra’ayi, da hanyoyin hana rikici tun daga tushe a matakin ƙasa.
A matsayinta na ƙungiyar gina zaman lafiya, CPSST ta sake jaddada jajircewarta wajen kare alfarmar rayuwa, zaman lafiya da haɗin kai, da gina al’umma inda babu wani iyali da zai fuskanci irin wannan raɗaɗin asara.
Muna tare da al’ummar Jihar Kano da dukkan ’yan Najeriya wajen neman adalci, tsaro, da zaman lafiya.
Sa hannu
Shugabanin Gudanarwa (Management)
Cibiyar Zaman Lafiya, Dorewar Ci Gaba da Jure Bambancin Ra’ayi (CPSST)